in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rivaldo ya bayyana niyar sa ta yin ritaya
2014-03-17 17:10:37 cri
Shahararren dan wasan kwallon kafar kasar Brazil mai suna Vítor Borba Ferreira, wanda aka fi sani da Rivaldo ya sanar ta shafinsa na Twitter cewa, daga ranar Asabar din da ta gabata ya yi ban kwana da taka kwallo. Rivaldo mai shekaru 41 da haihuwa, wanda kuma ke bugawa kulaf din Mogi Mirim wasa, ya fara taka leda ne tun a shekara ta 1996 a gasannin da kulaf din kasar Brazil ke bugawa. Ya kuma taba bugawa kuloflikan Deportivo, da Barcelona, da AC Milan wasa. Har wa yau wannan shahararren dan wasa ya taka leda a kulob din Cruzeiro, da Olympiacos, da AEK Athens, da kuma Bunyodkor na kasar Uzbekistan da sauransu.

Rivaldo ya taba kasancewa zakaran kwallon kafar nahiyar Turai, da kuma na duniya a shekarar 1999. A wancan lokacin tauraron wannan dan wasa ya haska matuka, inda ya kusa kaiwa ga shaharar da Ronaldo ya yi a fannin wasan kwallon kafa. Sai dai sabanin Ronaldo, Rivaldo ya fara neman samun 'yan kudaden shiga ne a lokutan wa'adin kwallon sa, inda da farko ya shiga kulob din Olympiacos na Greece, da kulob din AEK Athens. Kafin daga bisani ya koma kulob din Bunyodkor na Uzbekistan, da kulob din Kabuscorp na kasar Angola.

A shekarar 2012 kuma ya sake komawa Brazil. A ci gaba da buga kwallo inda Rivaldo ya shiga kulob din Mogi Mirim, wanda daga cikin sa ne kuma zai yi murabus. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China