in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Somaliya da AU sun kwace birni na 6 daga mayakan Al-Shabaab
2014-03-15 16:53:56 cri
Wata sanarwar da ta fito daga hedkwatar ofishin kungiyar AU ta ce rundunar hadin gwiwar dakarun gwamnatin kasar Somaliya ta SNA, da ta kungiyar AU dake kasar AMISOM, sun samu nasarar kwace birnin Buula Burde daga hannun mayakan Al-Shabaab bayan wani dauki ba dadi da sassan biyu suka yi.

Sanarwar ta ce birnin na Buula Burde wanda ke yankin Hiraan ya fada hannun dakarun dake biyayya ga gwamnatin kasar mai ci ne da yammacin ranar Alhamis, matakin da a cewar wakilin musamman na kungiyar AU, kuma jagoran tawagar AMISOM a Somaliyan Mahamat Saleh Annadif, wani babban ci gaba ne ga burin da ake da shi, na farfado da zaman lafiya da tsaro a kasar.

Buulu Burde dai ya zamo birni na 6 da tsagin gwamnatin kasar Somaliyan ya kwace cikin makwanni biyun baya bayan nan daga ikon kungiyar ta Al-Shabaab mai alaka da Al-Qaida, birnin da kuma ke da matukar muhimmanci ga kungiyar ta fuskar sansani da samar da kayayyakin bukata ga dakarun kungiyar. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China