in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Somaliya tace harin da aka kai ma fadar Shugaban kasar yaci tura
2014-02-21 20:46:27 cri
Ministan tsaron kasar Somaliya Abdelhakim Guled yace sojojin kasar sun dakile wani harin da aka kai a fadar Shugaban kasar a Mogadishu babban birnin kasar a jumma'an nan.

Wata mota mai dauke da bam ta tarwatse sannan aka biyo bayan wannan da jerin luguden harbe harbe a kusa da kofar arewacin fadar Shugaban kasar,abin da Guled yayi bayanin cewa sojojin kasar da taimakon sojojin kiyaye zaman lafiya na kungiyar Tarayyar kasashen Afrika AU sun kame magoya bayan kungiyar al shabbab da dama wadanda ake zargin da hannun su a cikin harin.

Manzon musamman na MDD a Somaliya Nicolas Kay wanda ya bayyana a shafin sa na twitter cewa shugaban kasar Hassan Sheik Mohamud na cikin koshin lafiya ya kuma yi allawadai da wannan harin a kan fadar shugaban kasar da ake kira Villa Somaliya. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China