in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi lale da cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Sudan ta Kudu
2014-01-24 11:50:39 cri
Babban sakataren MDD, Mista Ban Ki-Moon ya bayar da sanarwa ta bakin kakakinsa a jiya Alhamis, inda ya yi maraba da yadda sassa biyu da rikicin kasar Sudan ta Kudu ya shafa suka cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ya kuma kalubalanci sassan biyu da su tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar ba tare da bata lokaci ba.

A cikin sanarwar, Ban ya yi murnar nasarar cimma yarjejeniyar a karkashin sulhuntawar da kungiyar IGAD ta yi. Yanzu akwai bukatar a ci gaba da yin shawarwarin siyasa da zai kunshi wakilan 'yan siyasa da na sassa masu zaman kansu na kasar, da nufin cimma wata yarjejeniyar shimfida zaman lafiya a dukkan fannoni.

Ban da wannan kuma, Ban ya ce, MDD za ta kara kokarin da take yi na kiyaye fararen hula dake fuskantar hadari, da ba su taimakon jin kai da suka wajaba. Har illa yau dai, Ban ya kara yin kira ga sassa daban daban na kasar Sudan ta Kudu da su tabbatar da 'yancin tawagar musamman ta MDD dake kasar wato UNMISS, da ma'aikata masu aikin jin kai, da masu sa ido kan hakkin bil Adama wajen gudanar da ayyukansu a kasar. Kana kuma Ban ya yi yabawa da gwamnatin kasar Sudan ta Kudu saboda goyon bayan da ta baiwa UNMISS. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China