in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Sudan ta kudu ta sake kwato garin Bantio mai arzikin man fetur
2014-01-11 16:37:41 cri
A ranar jumma'a 10 ga wata sojojin Gwamnatin Sudan ta kudu ta samu nasarar sake kwato garin Bantio mai arzikin man fetur babban birnin jihar Unity daga hannun 'yan tawayen dake goyon bayan tsohon mataimakin shugaban kasar Reik Machar,kamar yadda kakakin sojin kasar ya sheda ma Xinhua.

Philip Aguer kakakin Sojin yace sojojin gwamnati bayan wannan nasarar na kwato duk garuruwan dake da arzikin man fetur a kasar yanzu haka tana kokarin ganin ta kwato garin Bor.

Anyi bata kashi sosai tsakanin bangarorin Machar dana Gwamnatin amma na gwamnati sunyi nasasa akan 'yan adawa inji Philip wanda baiyi wani bayani ba bayan hakan.

Garin Bantio yana da muhimmanci sosai a matsayin babban birnin jihar Unity wanda rijiyoyin man sa yake samar da ganga 45,000 a duk rana. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China