in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Aljeriya ya yi kira ga 'yan kasar da su yi kokarin kada kuri'arsu a zaben shugaban kasar
2014-03-03 10:58:25 cri
Shugaban kasar Aljeriya Abdelaziz ya bayar da wata sanarwa a ranar 2 ga wata, inda ya yi kira ga masu zabe na kasar da su yi kokarin kada kuri'arsu a zaben shugaban kasar da za a gudanar a watan Afrilu da ke tafe.

Shugaban a cikin sanarwar ya ce, ya kamata dukkanin masu zabe su yi kokarin kada kuri'arsu yayin zaben, su nuna goyon bayansu ga dan takarar da suka amince da shi. Ya kara da cewa, yadda masu zabe suka nuna himmarsu wajen kada kuri'ar shi ne zai kasance martanin da suka mayar ga wadanda suka lalata moriyar kasar, haka kuma ga wadanda ke nuna shakku kan ko al'ummar kasar suke da sanin ya kamata ta bangaren siyasa da kuma ko suna da karfin kiyaye kwanciyar hankali da tsaro a kasar ko a'a.

Za a gudanar da zaben shugaban kasar ta Aljeriya ne a ranar 17 ga watan Afril mai zuwa, kuma kawo yanzu, mutane sama da 130, ciki har da shugaban mai ci yanzu Abdelaziz Bouteflika ne, suka bayyana aniyarsu ta tsayawa takara a zaben.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China