in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi na kasar Sin ya bukaci daukar matakan gaggawa game da batun jirgin fasinjan kasar Malesiya
2014-03-08 15:44:14 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya bayyana bukatar daukar matakin gaggawa, don gano inda jirgin fasinjan nan na kasar Malesiya, mai dauke da fasinjoji 239 ya shiga.

Shugaba Xi, ya yi wannan kira ne a Asabar din nan, yana mai umartar ma'aikatar waje, da kuma ofisoshin jakadancin kasar sa, da hadin gwiwar kasashen da lamarin ya shafa, da su kara azamar gano inda wannan jirgi ya shiga. Ya ce ya zama wajibi, a yi duk mai yuwuwa, domin fuskantar yanayin da za a iya gamuwa da shi, da zarar an gano wannan jirgi.

Shi dai wannan jirgi kirar Boeing 777-200, ya taso daga birnin Kulala Lumpur na kasar ta Malesiya ne, zuwa nan birnin Beijing da sanyin safiyar Asabar din nan, ya kuma kamata ya iso birnin na Beijing da misalin karfe 6:30 na safe, amma kawo lokacin gabatar da labaran nan, ba a samu labarin inda ya shiga ba.

Rahotanni sun tabbatar da cewa wannan jirgi, na dauke da fasinjoji 'yan kasashe da dama, ciki hadda 'yan asalin kasar Sin 154. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China