in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na dora muhimmanci wajen koyar da fasahohi ga kasashen Afirka domin bunkasuwarsu
2014-02-20 20:46:13 cri
A yau Alhamis 20 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi ganawa da takwaransa na kasar Senegal, Macky Sall a nan birnin Beijing, inda suka kuduri niyyar kafa dangantakar abokantaka da hadin gwiwa tsakanin su cikin dogon lokaci, a kokarin sa kaimi ga bunkasuwar kasashen biyu tare.

Shugaba Xi ya bada shawarar cewa, ya kamata da farko manyan jami'an kasashen biyu su kara yin mu'amala tsakaninsu.sannan kuma su kara hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki, cinikayya, manyan kayayyaki na sufuri da sauransu. Sai kuma shawarar sa na uku da ya ce su kara hadin gwiwa wajen kyautata harkokin duniya da na shiyya-shiyya, a kokarin kiyaye moriyar kasashe masu tasowa.

Bayan haka, shugaba Xi ya kara da cewa, kasar tana goyon bayan kasashen Afirka wajen samun wata hanyar bunkasuwa data dace da yanayin da suke ciki.

A cewar shi kasar tana dora muhimmanci kan koyar da fasahohi ga kasashen Afirka, a kokarin cimma burin ganin sun samu bunkasuwa da kansu. Don haka Sin na fatan sa kaimi ga bunkasa sabuwar dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakaninta da kasashen Afirka zuwa wani sabon mataki tare da kasar Senegal.

A nasa bangare kuma, shugaba Sall ya bayyana cewa, Senegal na fatan kara hadin gwiwa tsakaninta da Sin a fannonin makamashi, manyan kayayyaki da zasu amfani jama'a, kayan amfanin gona da sauransu. Kuma kasar tana maraba da ganin Sin ta yi kokarin kafa cibiyar al'adun ta a Senegal tun da wuri. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China