in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bayyana matsayar ta akan yanayin da ake ciki a Ukraine
2014-03-03 20:46:54 cri
Kasar Sin ta ce matsayar data dauka akan yanayin da ake ciki yanzu a kasar Ukraine yana kan daidaici,gaskiya,adalci da kuma zaman lafiya.inji Kakakin ma'aikatar harkokin wajen ta Qin Gang.

Da yake amsa tambayoyi game da matsayin kasar Rasha a cikin wannan lamari, yace kasar Sin tana tsaye akan ka'idojin ta na diflomasiyya da tsarin huldar ta da kasashen waje kuma akan haka ne take tafiyar da al'amurran dake wakana a kasar Ukraine.

Mr Qin ya ce bayan haka kuma Sin tana bin yadda al'amurra suke a tarihi da dalilai na yanayin da ake ciki baki daya game da batun na kasar Ukraine wajen tsayawa a matsayin ta.

Wadannan bayanai dai sun zo ne a matsayin Karin haske game da bukatar kasar Sin da shi kakakin ma'aikatar harkokin wajen ya gabatar inda yace ya kamata duk bangarorin da lamarin Ukraine ya shafa su bi dokokin kasa da kasa wajen warware matsalar da suke fuskanta a siyasance ta hanyar tattaunawa da sulhu. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China