in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jagoranci taron kwamitin aiwatar da yin gyare-gyare
2014-02-28 21:11:24 cri
A yau ne kwamitin aiwatar da yin gyare-gyare na kasar Sin ya gudanar da taronsa na biyu, inda ya zayyana manyan abubuwan da zai mayar da hankali a kai yayin aiwatar da ayyukan gyare-gyare a shekarar 2014.

Taron wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jagoranta, ya amince da muhimmin kundin aikin da kwamitin zai gudanar na wannan shekara.

Bugu da kari, taron ya samu halartar Li Keqiang, Liu Yunshan da Zhang Gaoli da dukkan mambobin hukumar kula da harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na JKS.

Shugaba Xi ya bukaci shugabanni da su mayar da hankali kan abubuwan da ke kunshe cikin kudin kan wasu sassa na musamman kana su fito da bayanai ga jami'an da abin ya shafa da kuma lokacin da aka tsara.

Ya kuma jaddada cewa, wajibi ne a gudanar da aiki kamar yadda doka ta tsara yayin aiwatar da wadannan gyare-gyare, sannan wajibi ne duk wasu manyan canje-canje su dace da doka. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China