in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Ukraine ta bukaci kwamitin sulhu da ya tattauna halin da kasar ke ciki
2014-02-28 20:19:50 cri
Majalisar dokokin kasar Ukraine ta yi kira ga kwamitin sulhu na MDD da ya kira taron gaggawa don tattauna abin da ta kira mawuyacin halin da kasar da yaki ya daidaita ke ciki.

Bugu da kari majalisar dokokin kasar ta bukaci kasar Rasha da ta dakatar da abin da ta kira "zargin ceta cikakkun ikon kasar", kana kada ta goyi bayan raba kasar ta ko wane fanni.

A yau ne wasu gungun masu dauke da makamai suka kwace filin saukar jiragen saman birnin Simferopol, babban birnin Crimea da ke kudancin Ukraine, kwana guda bayan da 'yan bindiga suka kwace ginin majalisar dokokin birnin kana suka kafa tutar kasar Rasha a saman ginin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China