in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kebe ranar tunawa da kisan kiyashin Nanjing
2014-02-25 20:30:47 cri

Majalisar gudanarwar kasar Sin tana duba yiwuwar kebe ranar 3 ga watan Satumba a matsayin ranar da al'ummar kasar Sin suka nuna rashin amincewarsu kan mamayar da Japan ta yi wa yankunan kasar Sin.

Majalisar ta sanar da hakan ne a yau Talata, inda har ila take son ayyana ranar ta 13 ga watan Satumba a matsayin ranar tunawa da wadanda sojojin kasar ta Japan suka halaka a kisan kiyashin da suka aikata a birnin Nanjing a shekarun 1930.

Za a tattauna daftarin shawarar ce yayin taron kwamitin majalisar wakilan jama'ar Sin da ake gudanarwa sau biyu a wata, wanda za a gudanar daga ranar Talata zuwa ranar Alhamis.

Sojojin na Japan sun fara aikata wannan danyen aiki ne a Nanjing a ranar 13 ga watan Disamban shekarar 1937, inda suka halaka mutane sama da 300,000 cikin kwanaki 40. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China