in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta ce ba za ta martaba jami'ar Amurka mai kula da harkokin Tibet ba
2014-02-24 20:39:21 cri
Kasar Sin ta fito karara tana bayyana rashin amincewarta da matakin Amurka na nada wata jami'a ta musamman kan harkokin yankin Tibet na kasar Sin.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam, Hua Chunying ce ta bayyana hakan a yau Litinin yayin wani taron manema labarai.

Ta ce kasar Sin ba ta goyon wata kasar waje ta yi amfani da batun Tibet ta tsoma baki cikin harkokin cikin gidanta. Tana mai cewa, kasar Sin ba ta taba martaba wa ba kuma ba za ta yi hakan koda a nan gaba ba kan batun wai nada wata jami'a ta musamman kan batun yankin Tibet da kasar Amurka za ta yi,

Rahotanni na cewa, a ranar Jumma'a ce, Amurka ta nada jami'ar ta mai kula da harkokin da suka shafi hakkin bil-adama Sarah Sewall a matsayin jami'a ta musamman mai kula da harkokin yankin Tibet na kasar Sin. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China