in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tantance gawawwakin mutane 90 a garin Bama na Jihar Bornon Najeriya
2014-02-21 10:55:22 cri
Mahukunta a jihar Borno, dake Arewa maso Gabashin Najeriya, sun ce an tantance gawawwakin mutane 90, da harin garin Bama na ranar Laraba ya rutsa da su.

Rahotanni da kamfanin dillancin labarum kasar Sin Xinhua ya tattara, sun bayyana cewa, tuni jami'an karamar hukumar ta Bama suka mika gawawwakin mutanen ga iyalansu domin binne su.

Shi kuwa shugaban kungiyar 'yan aikin tsaro na sa kai dake yankin Akura Satomi, cewa ya yi mutane 96 ne kungiyarsa ta tantance, biyowa bayan harin da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne suka kaddamar da shi.

Baya ga wadanda suka rasa rayukansu, harin na garin Bama ya sabbaba jikkatar mutane da dama, tare da asarar dukiya mai tarin yawa, sakamakon kone gidaje, kantuna da tashar motar garin da maharani suka yi. Maharan sun kuma kai farmaki fadar hakimin Baman Kyari Ibn Ibrahim, koda yake dai ya tsira da ransa.

Tuni dai gwamnan jihar ta Borno Kashim Shettima, ya jaddada kira ga gwamnatin tarayyar kasar da ta fiddo da sabbin matakan dakile ayyukan kungiyar ta Boko Haram, wadda yanzu haka ke dada tsananta kai hare hare a sassan jihar daban daban. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China