in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya dakatar da gwamnan babban bankin kasar saboda sakaci ta hada hadar kudi
2014-02-20 20:32:40 cri
Rahotanni daga Najeriya a yau alhamis dinnan 20 ga wata sun nuna cewa Shugaban kasar Goodluck Jonathan ya dakatar da gwamnan babban bankin kasar Malam Sanusi Lamido Sanusi bisa zargin rashin bin abinda ya kamata,sakaci da hada hadar kudi abin da aka ce ya zama ruwan dare a lokacin jagorancin sa a wannan babban bankin kasar baki daya.

Kakakin fadar gwamnatin kasar Rueben Abati ya bayyana hakan da yake Karin haske akan lamarin ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Abuja babban birnin tarayyar kasar.

Mr Abati yace tuni aka umurci Malam Sanusi daya mika ragamar shugabancin bankin ga babbar mataimakiyar shi Mrs Sarah Alade,wadda zata rike kujerar har sai an gama binciken game da zargi yi ma dokoki zagon kasa,rashin bin kai'idojin tafiyar da harkokin bankin da salon mulkin da ake yi bankin.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China