in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron kolin kasashen Sahel a Nouakchott
2014-02-17 10:56:34 cri
A ranar 16 ga wata, a birnin Nouakchott hedkwatar kasar Mauritaniya ne, aka yi taron koli na kasashe 5 na yankin Sahel, inda shugabannin kasashen Mauritaniya, Mali, Niger, Chadi da Burkina Faso suka halarci taro na yini guda.

A yayin taron, shugabannin kasashen 5 sun tattauna batun tsaro da samun ci gaba, da yaki da ta'addanci, da sauran batutuwa. Bayan taron kuma, sun sanar da kafa kungiyar kasashe 5 na yankin Sahel don inganta hadin gwiwa a wannan yanki, kuma shugaban kasar Mauritaniya Mohamed Ould Abdel Aziz ya kasance shugaban karba-karba na farko na kungiyar, kuma an kafa sakatariyar a birnin Nouakchott da ke kasar Mauritaniya.

A gun taron manema labaru da aka shirya bayan taron, Aziz ya bayyana cewa, makasudin kafa wannan sabuwar kungiya shi ne, domin yaki da ta'addanci. Ya jaddada cewa, cimma burin samar da tsaro da zaman lafiya shi ne babban aikin wannan kungiya, kuma sai da tsaro kafin a samu sahihin ci gaba. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China