in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan Zambiya sun harbe wadansu "yan fashi uku har lahira da suka yi fashi a wajen aikin wassu Sinawa
2014-02-16 16:27:30 cri
'Yan Sandan kasar Zambiya sun harbe wassu 'Yan fashi su uku har lahira da suka yima wani ma'aikata na Sinawa fashi,kamar yadda ofishin jakadancin kasar Sin a Lusaka da kuma majiyar 'Yan sanda suka tabbatar.

'Yan sanda a nan take suka kaddamar da farautar 'yan fashin bayan da aka kai masu rahoto kuma sakamakon haka aka gano su sannan ba tare da bata lokaci ba aka harbe su a wannan dare.

Mataimakin kwamishinan 'yan sanda a Lusaka,Nelson Phir yayi bayanin cewa a lokacin da aka gano su an samu manyan bindigogin AK47 guda biyu tare da su da kuma wata karamar motar shiga.

Mr Nelson Phir yayi bayanin cewa an samu shaidu masu kwari dake nuna cewa wadannan mutane su ne suka yi fashin a safiyar ranar laraba a ma'aikatan hakar kwaru dake wajen birnin Lusaka abinda yayi sanadin jikkatar Sinawa 7, daga baya daya daga cikin su ya mutu a asibiti saboda mummunan raunin da ya samu. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China