in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kananan girgizar kasa sama da sau 1700 a jihar Xinjiang
2014-02-14 20:21:32 cri
A yau ne hukumar kula da girgizar kasa ta jihar Xinjiang ta kasar Sin ta bayyana cewa, zuwa karfe 10 na wannan rana, baki daya an yi kananan girgizar kasa sama da sau 1700 a jihar Xinjiang, a cikinsu wanda ya fi tsanani har karfinsa ya kai maki 5.7 bisa ma'aunin Richter. Yawan mutanen dake fama da bala'in ya kai sama da dubu 50. Kawo yanzu dai, babu wani rahoton cewa akwai mutanen da suka mutu ko kuma jikkata sakamakon hadarin.

Mataimakin darektan ofishin samar da taimakon gaggawa na jihar Xinjiang, Zhao Yan ya bayyana cewa, bisa yanayin da ake ciki yanzu, mafi yawan gidajen da suka lalace tsoffi ne. Mataimakin shugaban hukumar kula da girgizar kasa ta jihar Xinjiang, Zhang Yong ya furta cewa, ya zuwa karshen shekarar bara, an kafa gidajen da za su iya jure girgizar kasa kimanin miliyan 3 a jihar Xinjiang, kuma ya zuwa yanzu kimanin kashi 80% na makiyayan jiyar sun samu damar zama a wadannan gidaje masu inganci.

Kawo yanzu, hukumar kula da harkokin jama'a ta jihar Xinjiang mai cin gashin kanta ta samar da kayayyakin ceto zuwa yankin da ke fama da bala'in cikin gaggawa, tare da tsugunar da mutanen da bala'in ya ritsar da su.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China