in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kongo (Brazaville) ta yi shirin kafa asusun nuna goyon baya ga sake gina Afrika
2014-02-12 14:49:39 cri
A ranar 11 ga wata, shugaban kasar Kongo (Brazaville) Denis sassou-nguesso ya sanar da cewa, za a kafa wani asusun zaman lafiya don nuna goyon baya game da aikin sake gina kasashen Afrika bayan yake yake.

A wannan rana, yayin da Sassou ke halartar bikin cika shekaru 25 da amfani da yarjejeniyar Brazaville a hedkwatar kasar, ya bayyana cewa, yanzu, jama'ar kasar Afrika ta Tsakiya na shan wahala, kasashen duniya na da hakkin ci gaba da daukar matakai, don kawo karshen rikici a cikin wannan kasa. Ya sanar da cewa, za a kafa wani asusun zaman lafiya, don nuna goyon baya game da aikin sake gina yankunan kasashen Afrika da ke fama da yake-yake.

A ranar 13 ga watan Disamba na shekarar 1988, kasashen Angola, Cuba, da Afrika ta kudu sun daddale wata yarjejeniya a birnin Brazaville, inda suka amince da bin ka'idar warware rikici a yankunan yammaci da kudancin Afrika cikin lumana, don kawo karshen rikice rikicen soja da ake fama a shiyyar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China