in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nuna adawa ga rokon da kasar Philippines ta yi na neman sulhuntawa a kotun kasa da kasa game da harkokin teku
2013-02-21 17:01:05 cri
A ranar 20 ga wata, ma'aikatar harkokin wajen kasar Philippines ta bayyana cewa, nan ba da dadewa ba, Philippines za ta mika rokon neman sulhuntawa ga babbar kotun binciken laifuffukan da suka shafi harkokin teku ta kasa da kasa, game da rikicin da ke tsakaninta da kasar Sin don gane da yankunan tekun kudu.

A wannan rana kuma, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana cewa, kasashen Sin da Philippines, kasashe ne da suka rattaba hannu kan yarjejeniya game da tekun kudu, kuma kamata ya yi su bi alkawarin da suka dauka cikin yarjejeniyar a tsanake, haka nan kuma Hong Lei ya jaddada cewa, Sin ba ta amince da matakan da Philippines za ta dauka na neman sulhuntawa a kotun kasa da kasa ba, kuma ta bayyana adawar ta karara ga wannan lamari. Hong Lei ya kuma jaddada cewa, Sin ta tsaya kan ra'ayinta cewa, ya kamata a tsaya ga bin tsarin yin shawarwari wanda akasarin kasashen da ke wannan yanki na nuna goyon baya a halin yanzu, kuma Sin za ta ci gaba da kokari don kiyaye zaman lafiya da karko a yankin tekun kudu, da tsayawa tsayin daka wajen tabbatar da mulkin kai da moriyar kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China