in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na son hadin kai tare da bangarori daban daban don tabbatar da zaman lafiya a tekun dake kudu da kasar
2012-09-04 20:59:06 cri
Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya furta a nan birnin Beijing a yau Talata 4 ga wata cewa, kasar Sin na fatan ganin bangarorin da batun tekun dake kudu da kasar Sin ya shafa su tsaya kan yarjejeniyar da suka cimma, da kara amincewa a tsakaninsu, da kara azama kan hadin gwiwarsu, ta yadda za a samu damar magance ayyukan da ka iya lalata yanayin da ake ciki, da kuma tabbatar da zaman lafiya a wannan yankin.

Hong ya ce, tun daga farkon wannan shekara, kasar Sin da kasashen membobin kungiyar tarayyar kasashen kudu maso gabashin Asiya sun shirya tarurukan manyan jami'ai guda 2, inda bangarori daban daban suka cimma daidaito kan aiwatar da yarjejeniyar da aka kulla wadda ta kayyade matakan da za a dauka dangane da batun yankin tekun dake kudu da kasar Sin.

Ban da haka kuma, bangarorin da batun da ya shafa na kokarin tsara wata doka game da haka. A cewar Hong, kasar Sin a nata bangare tana fatan ganin sauran kasashe za su girmama kokarin da kasar Sin da kasashen kudu maso gabashin Asiya suka yi, sa'an nan su kara daukar wasu matakai da za su taimakawa kara aminci da tabbatar da kwanciyar hankali.

Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin tana sane da cewa kasar Amurka ta taba bayyana matsayinta na 'yan ba ruwan mu dangane da cece-kuce da ake yi kan ikon mallakar tekun dake kudu da kasar Sin, don haka kasar Sin na fatan ganin Amurka za ta tsaya kan maganarta, kana ta kara gudanar da wasu ayyukan da za su taimaka wajen samar da zaman lafiya a wannan yankin. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China