in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya yi Allah wadai da kisan wani ma'aikacin MONUSCO
2014-02-06 16:32:30 cri
Wakili na musamman ga babban magatakardan MDD a jamhuriyar dimokaradiyyar Congo Martin Kobler, ya yi tir da kisan wani ma'aikacin rundunar wanzar da zaman lafiya ta MONUSCO. Mr Kobler ya kuma yi kira ga mahukuntan kasar ta Congo da su gaggauta gudanar da bincike da nufin hukunta wanda duk ke da hannu cikin wannan ta'asa.

Mukaddashin mataimakin kakakin MDD Farhan Haq ne ya rawaito wannan tsokaci na Mr. Kobler, yayin taron ganawa da 'yan jarida na rana rana da ya gabata a ranar Laraba.

Wata sanarwa daga rundunar ta MONUSCO dai ta bayyana cewa, an harbe ma'aikacin ne a hanyarsa ta zuwa wurin aiki da sanyin safiyar ranar Larabar, a birnin Beni dake yankin Arewa maso Gabashin kasar ta Congo, yankin da ke ci gaba da fama da yawan tashe tashen hankula. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China