in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta goyi bayan sojojin Congo wajen kafa yankin tsaro a gabashin DRC
2013-07-31 09:59:34 cri
Ofishin MDD mai kula da wanzar da zaman lafiya a Jamhuriyar Demokuradiyar Kongo, wato MUNOSCO zai goyi bayan sojojin Kongo wajen kafa yankin tsaro a shiyyar Goma, wani babban gari a gabashin kasar da kuma wanda ke ta arewacin kasar, in ji kakakin majalissar a ranar Talatar nan 30 ga wata.

Ofishin ya yanke shawarar hakan ne sakamakon babban hadarin da fararen hula ke fuskanta a yankin Goma-Sake dake arewacin Kivu, kamar yadda mataimakin kakakin majalissar Eduardo Del Buey ya yi bayani ma manema labarai.

A cikin bayanin Majalissar, ta ce tun tsakiyar watan Mayu, wannan yankin yake fuskantar hare hare daga wajen 'yan tawaye na M23 a kan sansanin sojojin kasar Kongo, abin da ke nuna cewa suna son kutsa kai a cikin garin na Goma da Sake.

A bayaninsa wannan hare hare na bayan bayan nan da aka fara shi daga ranar 14 ga watan Yulin nan, kungiyar 'yan tawayen sun yi amfani da manyan makamai inda suka bude wuta ba kakkautawa ta ko'ina, abin da ya yi sanadiyyar hasarar rayukan fararen hula da dama, kuma har ila yau harin ya shafi cibiyoyin MDD.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China