in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kiran tabbatar da wucewar 'yan gudun hijra DR Congo ba tare da wani hadari ba
2013-07-20 15:58:59 cri
Mai magana da yawun MDD Martin Nesirky ya baiyana cewar wasu cibiyoyin MDD sun yi kira ranar Jumma'a ga dukkan masu dauke da makamai da su tabbatar 'yan gudun hijra dake kaura daga Jamhuriyar demokradiyar Congo (DRC) saboda fadace-fadace sun samu wucewa ba tare da wani hadari ba.

Nesirky ya ce babban darektan cibiyar abinci ta duniya (WFP) Ertharin Cousin ya yi kira ga masu dauke da makamai su tabbatar da cewa kungigoyin tallafawa bil adama sun samu damar taimakawa jama'a mabukata, kuma a duk inda suke a cikin kasar.

An samu dakatar da fada da ya sake barkewa ranar Lahadi tsakanin dakarun gwamnati da na kungiyar 'yan tawayen M23 a wajen garin Kanyaruchiya, mai nisan kusan kilomita 15 da Goma, babban birnin yankin arewacin Kivu, in ji hukumar kawo daidaito a Jamhuriyar Demokrdaiyar Congo ta MDD (MONUSCO).

Hukumar ta baiyana a cikin wani rahoto cewa koda yake kura ta lafa, har yanzu ana zaman dar-dar a Goma.

A yayin jawabi ga manema labarai da aka saba yi kullum, Nesirky ya ce Mr Cousin ya kai ziyara Congo DRC a wannan mako, inda ya kara jadadda cewa manufa daya ta hukumomin MDD da sauran abokan aikinsu daga cibiyoyi da ba na gwamnati ba shi ne samar da tallafin ceton rai ga jama'a mabukata. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China