in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari ga wani kurkukun dake cibiyar babban birnin kasar Nijer
2013-06-02 16:49:18 cri
A ranar Asabar 1 ga wata da yamma, wasu dakarun da ake zargin membobin kungiyar masu Jihadi ta yammacin Afirka ne suka kai wani kurkuku hari dake Niamey, babban birnin Jamhuriyar Nijer, lamarin da ya haddasa mutuwar 'yan sanda a kalla 2.

Bayan abkuwar lamarin, 'yan sandan kasar, sun kange hanyoyin da ake bi zuwa kurkukun, kana sun kewaye wurin.

Akwai membobin kungiyar Boko Haram da dama a cikin wannan kurkuku.

Ministan kula da harkokin dokokin shari'a na kasar Nijer Marou Amadou ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu, ba a san ko akwai alaka tsakanin wannan lamari da lamarin fashewar boma-boman kunar bakin wake da ya faru a ranar 23 ga watan Mayun da ya gabata a kasar ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China