in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Nijar da Guinee-Equatoriale na kokarin inganta dangantakarsu domin bunkasa musaya
2013-07-26 11:06:51 cri
Kamar yadda aka tsaida a takardun hadin gwiwa da aka rattaba hannu tsakanin ta da hukumomin Malabo, kasar Nijar ta dauki niyyar tura kayayyakin noma da kiyo zuwa kasar Guinee-Equatoriale, musammam ma nama, albasa, tafarnuwa da kuma dankalin turawa, a cewar wata sanarwa da ta fito daga hukumomin kasar Nijar a birnin Yamai.

A cewar wannan sanarwa ta gwamnatin kasar Nijar da ta fito bayan wani zaman taron ministoci da aka shirya a ranar Laraba a birnin Yamai, kamar yadda aka tsara bisa tushen takardun hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, ton hamsin na nama ne kasar Nijar za ta rika tura wa kasar Guinee-Equatoriale sau biyu a ko wane wata.

Tuni manyan 'yan kasuwa na kasashen biyu suka yi shirin rattaba hannu kan takardun kwagilar kasuwanci da za su kasance wani matakin aza harsashi, da kuma matakan yadda za'a rika biyan kudi, da yadda za a fitar da su bisa amincewar bangarorin biyu.

Wata tawagar aiki ta ma'aikatar kiyon kasar Nijar za ta isa birnin Malabo nan bada jimawa ba, domin kara azama kan ayyukan da aka tsaida bisa tushen yarjejeniyoyin da kasashen biyu suka sanya wa hannu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China