in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin Nijar sun bukaci mutanen kasar dasu bada kulawa ga fasahar nakasassu
2013-08-01 13:05:04 cri
Ministar kula da al'umma ta kasar Nijar, madam Maikibi Kadidiatou Dandobi a ranar Laraba ta yi kira ga mutanen kasar Nijar da su maida hankali tare da fifita fasahar nakasassu ta hanyar sayen kayayyakin da suka sarrafawa da kansu, ta yadda za'a bunkasa wannan sana'a tasu a cikin gida da kasashen waje.

Madam Kididiatou Dandobi ta yi wannan jawabi a yayin bikin ranar nakasassu ta kasa karo na 21 da aka gudanar a ranar Laraba, bisa taken "Karfin bada kulawa ga fasahar nakasassu, wani muradi na cigaban kasar Nijar".

A cewar wannan jami'a, kasar Nijar na daya daga cikin kasashen shiyyar yammacin Afrika da ta tanadi makaman dokoki don kare nakasassu kuma kasa ta farko ta sanya hannu kan yarjejeniyar kare mutunci da 'yancin nakasassu a ranar 24 ga watan Yunin shekarar 2008. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China