in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sham da 'yan adawa sun yi shawarwari gaba da gaba
2014-01-25 20:26:35 cri
Gwamnatin kasar Sham da masu adawa da ita sun yi shawarwari gaba da gaba a ranar Asabar din nan, lamarin da ya zama irin ganawar karo na farko tun bayan da bangarorin 2 suka fara yaki da juna shekaru 3 da suka wuce.

Wata majiya daga ofishin watsa labarai na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva ta bayyana haka ga wakilin Xinhua, kamfanin dillancin labarai na kasar Sin, inda ta yi bayanin cewa, bangarorin 2 a halin yanzu suna tattaunawa tare da manzon musamman mai kula da batun Sham mista Lakhdar Brahimi, a ofishin MDD dake Geneva.

Hakan ya zama karo na farko ke nan da bangarorin 2 suka gana gaba da gaba a shekaru 3 da suka wuce, duk da cewa sun nuna shakku lokacin da aka fara taron Geneva karon na 2 a ranar Laraba a Montreux na kasar Swiss. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China