in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya nuna farin cikin ganin kungiyar adawa ta kasar Sham za ta halarci taron Geneva na 2
2014-01-19 16:36:18 cri
Ban Ki-moon, babban sakataren MDD, ya ba da sanarwa ta kakakinsa a ranar 18 ga wata cewa, ya yi farin ciki kan yadda babbar kungiyar adawa ta kasar Sham dake ketare NCSROF ta tsai da kudurin halartar taron Geneva karo na 2 kan rikicin Sham.

Mista Ban ya bayyana cewa, kudurin da aka tsayar ya kasance wani babban ci gaba a kokarin daidaita rikicin kasar ta hanyar shawarwari da dabarun siyasa, sa'an nan yana son ganin kungiyoyin dake adawa da gwanatin kasar Syria sun gaggauta wajen kafa wata tawagar da za ta wakilci dukkansu wajen wannan taron.

Kungiyar NCSROF ta sanar a ranar 18 a birnin Istanbul na kasar Turkiya da cewa, za ta halarci taron Geneva na 2 kan Sham da za a kira a ranar 22 ga wata. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China