in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Iran ta tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a taron Geneva
2014-01-13 20:36:28 cri
Rahotanni daga kasar Iran sun ruwaito mai shiga tsakani na kasar game da batun nukiliyar kasar Abbas Araqchi na tabbatar da cewa, kasar ta Iran da kasashen nan shida da batun nukiliyar kasar ya shafa, sun amince su fara aiwatar da yarjejeniyar Geneva da suka cimma tun daga ranar 20 ga watan Janairu.

Ya ce, an cimma kaiwa ga daddale yarjejeniyar ce da Helga Schmid, mataimakin Catherine Ashton, shugabar kungiyar EU mai kula da harkokin diflomasiya da tsaro, bayan ganawar kwararru ta baya-bayan game da aiwatar da yarjejeniyar nukiliyar da aka kammala a ranar Jumma'a.

Da zarar kasar ta Iran ta aiwatar da wannan yarjejeniya, kasashen 6, wato Amurka, Burtaniya, Faransa, Rasha, Sin da kuma Jamus za su yi kokarin ganin an fara sassauta takunkumin da aka kakabawa kasar ta Iran.

Jami'in kasar Iran din ya bayyana cewa, kasar a shirye take ta bar tawagar hukumar IAEA ta fara duba ko kasar ta Iran ta fara aiwatar da wannan yarjejeniya tun daga ranar 20 ga watan Janairu ko a'a. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China