in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a ci gaba da warware batun nukiliyar Iran ta hanyar yin shawarwarin siyasa, in ji kasar Sin
2013-12-16 20:47:37 cri
Yau Litinin 16 ga wata ne, kakakin ma'aitakar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a birnin Beijing cewa, kasar Sin za ta ci gaba da sa kaimi ga bangarori daban daban da batun nukiliyar kasar Iran ya shafa wajen ci gaba da shawarwarin tsakaninsu don ba da gudummawa wajen warware batun bisa dukkan fannoni yadda ya kamata.

Bisa labarin da muka samu, an ce, a ran Lahadi 15 ga wata, yayin da yake tsokaci kan karin takunkumin da kasar Amurka ta kakabawa kasar Iran, ministan harkokin wajen kasar Iran Mohammad Javad Zarif ya bayyana cewa, tun lokacin da aka fara shawarwari kan batun nukiliyar kasar, ya fahimci cewa, shawarwarin abu ne mai wahala dake daukar dogon lokaci, kana kasar Iran za ta ci gaba da shawarwarin da take yi da kasashen nan shida dake shafar batun nukiliyar kasar.

Kan lamarin, Ms. Hua Chunying ta bayyana cewa, a halin yanzu, ya kamata bangarori daban daban da abin ya shafa su dukufa wajen warware batun nukiliyar kasar Iran ta hanyar shawarwarin siyasa bisa ka'idojin girmama juna da kuma nuna adalci ta yadda za a iya ciyar da wannan aiki gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China