in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yaba wa kokarin dukkan bangagorin da suka shiga aikin jigilar makamai masu guba na Syria
2014-01-14 18:45:30 cri
Kasar Sin ta yaba wa kokarin dukkan bangaorin da suka shiga aikin jigilar makamai masu guba na kasar Syria, ciki har da gwamnatin kasar ta Syria.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ne ya bayyana hakan ranar Talata, yayin da yake bayani ga manema labarai game da yadda aka kammala matakin farko na aikin jigilar makamai masu guba na kasar ta Syria.

Hong Lei ya ce, gwamnatin Syria ta aiwatar da shawarwarin kungiyar haramta amfani da makamai masu guba ta duniya (OPCW) da kudurorin MDD yadda ya kamata, ta hanyar kammala zagayen farko na jigilar makamanta masu guba ranar Talata da ta gabata.

Ya ce sauran kasashe ciki har da Sin, Rasha da Denmark, hakika sun taka rawa don tabbatar da cewa, aikin ya gudana lami lafiya.

Mr. Hong ya ce, aikin jigilar makamai masu guba, wani muhimmin mataki na kaiwa ga lalata su, kuma kasar Sin za ta hada kai da sauran bangarori don ganin abubuwa sun gudana kamar yadda aka tsara. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China