in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a lalata makamai masu guba na Syria tun da wuri, in ji Ban Ki-moon
2013-12-29 16:46:01 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayyana a ranar Asabar cewa, ko da yake an jinkirtar aikin jigilar da lalata wasu makamai masu guba daga Syria, amma kungiyar hana yaduwar makamai masu guba OPCW ta hadaddiyar tawagar MDD za ta ci gaba da aikinta, domin jigilar makaman daga Syria da kuma lalata su tun da wuri.

Sanarwar ta ce, mai shiga tsakani na musamman na kungiyar OPCW ya nuna a wannan rana cewa, za a jinkirta aikin jigilar makamai masu guba a karo na farko daga Syria bisa ga shirin da aka tsara, tare da bayyana cewa za a kammala shi kafin ranar 31 ga wata a sakamakon wasu dalilai. Amma Ban Ki-moon ya jaddada cewa, kokarin kasashen duniya na kawar da makamai masu guba na Syria na samun ci gaba a ko da yaushe, cikin watanni uku da suka wuce, an cimma dukkan muhimman ayyukan a wannan fanni yadda ya kamata. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China