in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran za ta ci gaba da inganta dangantakar hadin gwiwa da kasar Iraqi
2013-12-06 16:39:52 cri
Shugaban kasar Iran Hassan Rohani ya bayyana cewa, gwamnatin sa na fatan ci gaba da inganta dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni da makwafciyar ta wato kasar Iraqi.

Shugaba Rohani ya furta hakan ne a ranar Alhamis 5 ga watan nan a birnin Tehran hedkwatar kasar ta Iran, yayin ganawarsa da firaministan kasar Iraqi Nuri Kamal al-Maliki, wanda ke ziyarar aiki a kasar ta Iran.

Bisa sanarwar da wata kafar yanar gizo ta fitar, an ce yayin ganawar jagororin biyu shugaban kasar Iran ya bayyana bukatar inganta dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Iran da Iraqi, tare da binciko hanyoyin cimma moriyar juna cikin dogon lokaci, musamman ma a fannin tattalin arziki, da samar da muhimman ababen more rayuwa.

Yayin da aka tabo batun kasar Siriya kuwa, shugaba Rohani ya ce ya kamata taron Geneva karo na 2 game da batun Siriya, wanda za a shirya nan ba da dadewa ba, ya taimakawa kasar wajen shirya babban zabe cikin 'yanci, kuma ba tare da gindaya wani sharadi ba.

A nasa tsokaci, Firaminista Maliki, ya bayyana farin cikin sa bisa nasarar da aka samu ta cimma matsaya guda a mataki na farko tsakanin Iran da kasashe 6 da batun nukiliyar ta ya shafa. Ya ce, ya yi imanin cewa, kokarin da gwamnatin Iran take yi, zai bada damar warware batutuwa na wannan yanki baki daya.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China