in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe wani mataimakin ministan masana'antun kasar Libya
2014-01-12 20:35:34 cri
A ranar jiya da dare, rahotonni daga kasar Libiya sun bayyana cewa mataimakin ministan masana'antu na gwamnatin wucin gadin kasar Libya Hassan Ali Droui ya rasu a birnin Sirte dake gabashin birnin Tripoli, a cikin wani farmakin da wasu 'yan ta'adda da ba a tantance su ba suka kai masa.

Wani jami'in tsaron gwamnatin kasar ya bayyana cewa, a wannan rana da dare, 'yan ta'adda sun kai wa mista Droui hari kusa da kasuwar dake cibiyar birnin Sirte, inda suka lugudan wuta kan motar dake ciki tare da kashe shi.

Birnin Sirte shi ne yankin marigayi shugaban kasar Moammar Gadhafi, tun bayan yakin basasa tare da kifar da gwamnatinsa, har yanzu ana samun dakarun dake adawa da sabbin hukumomin kasar ta Libiya, lamarin dake kawo zaman zullumi a wannan yanki tun bayan rikicin kasar. Mista Droui shi ne mataimakin ministan masana'antun kasa, kuma ya taba zama mamban kwamitin wucin gadi na kasar Libya dake yankin Sirte. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China