Dakarun gwamnatin sun samu nasarar fara kutsawa birnin ne, yayin da 'yan tawayen suka amince su fara tattaunawa da nufin cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta tare da kawo karshen tashin hankalin da ya barke ranar 15 ga watan Disamba a wannan jaririyar kasa.
Kafar yada labarun Sudan Tribune ta ruwaito kakakin sojojin Sudan ta kudu Philip Aguer na tabbatar da wannan labarin, kana sojojin sun himmatu wajen ganin sun sake kwato garin Bantio, babban birnin jihar Unity mai arzikin mai da 'yan tawayen ke rike da shi. (Ibrahim)