in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta lalata haramtattun hauren giwa har tan 6.1
2014-01-06 19:40:49 cri

Rahotanni daga birnin Dongguan na lardin Guangdong dake kudancin kasar Sin na nuna cewa gwamnatin kasar ta lalata haramtattun hauren giwa data kwace a ranar litinin din nan 6 ga wata.

Bikin lalata hauren giwan wanda shi ne karo na farko a kasar Sin,ya nuna kokarin da gwamnati take yi na hana cinikin hauren giwa bada izini ba,da kuma bukatar dake akwai na wayar da kan jama'a wajen kare namun daji.

Hauren giwayen da ba'a kai ga sarrafa su ba da kuma wadanda aka riga aka kankare aka yi ma ado wadanda gwamnati ta kwace a cikin shekarun da suka gabata an tara su gu daya ne tare da nike su.

Wannan aikin dai hukumar kula da gandun daji da sha'anin mulki na shige da fice na kasar ta gudanar. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China