in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar bincike kan makamai masu guba ta MDD ta bar birnin Damascus
2013-08-31 20:55:42 cri
Tawagar kwararru masu bincike kan makamai masu guba ta MDD ta bar Damascus, babban birnin kasar Sham ko Syria, a yau Asabar 31 ga wata, inda kuma ta nufi birnin Hague na kasar Holland, dauke da samfurin sinadarai da ta tattara daga Syria.

A jiya Juma'a ne dai, kakakin babban sakataren MDD Martin Nesirky ya bayyana cewa, tawagar binciken ta riga ta kammala ayyukanta, ciki hadda bincikar zargin da ake yi cewa, an yi amfani da makamai masu guba kan fararen hula a kasar ta Syria a ran 21 ga watan nan.

(Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China