in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi a daidaita batun Syria karkashin kulawar MDD, in ji kasar Sin
2013-09-17 20:18:46 cri
A ranar Litinin 16 ga wata, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya ba da rahoton bincike a kan makamai masu guba na Syria ga kwamitin sulhu na MDD, wanda ya nuna cewa, lallai an yi amfani da makamai masu guba yayin rikici tsakanin bangarori daban daban na Syria, amma ba tare da fallasa wa ya yi hakan ba. Game da wannan batu, a yau Talata 17 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Hong Lei ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, Sin ta yaba wa rukunin bincike na MDD wajen gudanar da aikinsa cikin mawuyacin hali, tare da dora muhimmanci da yin nazari kan abubuwan dake kunshe a rahoton.

Hong ya ce, a bayyane yake cewa Sin tana tsayawa tsayin daka kan matsayin da ta dauka dangane da makamai masu guba. Sin ba za ta amince ma kowa ba wajen amfani da su, kuma da babbar murya ta yi Allah wadai da wadanda suka taba amfani da makamai masu guba a Syria. Ya jaddada cewa, Sin tana goyon bayan rukunin MDD wajen ci gaba da aikinsa bisa yarjejeniya tsakaninsa da gwamnatin Syria. Kuma Sin na maraba da yarjejeniyar da Amurka da Rasha suka daddale, da nuna goyon baya ga soma aikin lalata makamai masu guba na Syria karkashin kulawar MDD, tare da sa kaimi ga yunkurin daidaita batun a siyasance.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China