in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MONUSCO ta samar da taimakon jin kai ga tsoffin mayaka a kasar Congo Kinshasa
2013-12-29 16:39:37 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD a kasar Congo (MONUSCO) ta samar wa gwamnatin Congo Kinshasa a kwanakin nan da taimakon jin kai na abinci da kuma wanda ba na abinci ba ga tsoffin mayakan da aka jibge a sansanin Bweremana dake fiye da kilomita 40 daga birnin Goma, hedkwatar arewacin Kivu a wani labarin da ya fito daga rundunar sojojin kasar.

Taimakon jin kan ya hada da katifu 900, abinci kusan ton goma da kuma barguna fiye da 2000, in ji manjo janar Tim Mukunto, wani babban jami'in rundunar sojojin kasar ta takwas FARDC, tare da bayyana cewa wannan taimako ya zo domin kara wa bisa kokarin da gwamnatin kasar take bisa tsarin ba da kulawa ga tsoffin mayaka bisa yarjejeniyar karbe makamai ta Congo Kinshasa.

MONUSCO da kungiyoyin MDD dake kasar Congo Kinshasa sun nuna damuwa kan halin zaman rayuwa na wadannan tsoffin 'yan tawaye dake sansanin Bweremana da aka kiyasta yawansu zuwa fiye da 11,140 inda aka hada 2,600 na tsoffin mayakan kungiyoyin masu makamai da suka fito daga kasashen waje da aka tsugunar dasu zuwa yankuna uku Kitona a gundumar Bas-Congo, Kamina a yankin Katanga da kuma Kotakoli a yankin Equateur. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China