in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta kaddamar da wani jirgi maras matuki a jamhuriyar dimokaradiyyar Congo
2013-12-04 09:44:53 cri
Rahotanni daga birnin Goma dake Gabashin jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, na cewa MDD ta jagoranci harba wani jirgin sama na tsaro maras matuki, domin aikin sanya ido ga yankunan fararen hula.

Kakakin ofishin MDDr Martin Nesirky ne ya tabbatar da hakan, yayin ganawar sa da 'yan jaridu. Nesirky ya kara da cewa ana sa ran amfani da wannan jirgin sama ne domin ba da kariya ga fararen hula dake yankunan gabashin kasar masu fama da yawan tashe-tsahen hankula.

Manyan jami'an MDD, ciki hadda karamin sakatare mai lura da harkokin wanzar da zaman lafiya a kasar Herve Ladsous, da wakilin babban magatakardar MDD a kasar Martin Kobler, sun halarci bikin kaddamar da wannan jirgi.

Da yake jawabi bayan kaddamar da harba jirgin Mr. Ladsous ya ce wannan ne karon farko da ofishin MDD zai yi amfani da irin wannan jirgi domin aikin wanzar da zaman lafiya, wanda kuma zai yi matukar tallafawa aikin da tawagar MONUSCO ke yi, musamman ma wajen karade dukkanin sassan da ake bukatar sanya ido kan su.

A baya bayan nan dai dakarun sojin kasar Congo, da hadin gwiwar tawagar ta MONUSCO sun samu nasarar karya lagon kungiyar 'yan tawaye kasar ta M23, wadda a baya ta mamaye lardin Arewacin Kivu, matakin da ya tilasa M23r ajiye makamai. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China