in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka za ta tura sojoji zuwa kasar Sudan ta Kudu don kiyaye 'yan kasar ta
2013-12-21 17:24:58 cri
Sakamakon halin dar dar da ake ciki a kasar Sudan ta Kudu, shugaba Barack Obama na Amurka, ya aike da wata wasika ga majalisar dokokin kasa, inda ya bayyana cewa, ya riga ya aike da sojoji 45 zuwa kasar Sudan ta Kudu a ranar 18 ga wata.

Wasikar ta bayyana kiyaye tsaron rayuka da dukiyoyin 'yan asalin kasar ta Amurka, a matsayin babban dalilin aikewa da dakarun. An kuma ce wadannan sojoji za su koma Amurka da zarar al'amura sun daidai ta a kasar.

Cikin 'yan makwannin nan dai, tashe-tsahen hankula a kasar Sudan ta Kudu sun haddasa mutuwar mutane kimanin dubu guda. Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir ya zargi tsohon ma'aimakin sa Riek Machar da shirya juyin mulki, wanda daga baya ya janyo dauki ba dadi tsakanin sassan kasar da basa ga maciji da juna, koda yake dai Machar ya karyata wannan zargi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China