in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Masar ta sanar da soke dokar ta baci da dokar hana fitar dare tun daga ranar 14 ga wata
2013-11-03 16:43:36 cri
Bisa labarin da aka bayar a shafin internet na jaridar Al-Ahram ta kasar Masar a ranar 2 ga wata, an ce, majalisar ministocin kasar ta sanar da soke halin dokar ta baci a dukkan kasar tun daga ranar 14 ga wata, kana za a soke dokar hana fitar dare dake aiki a jihohi 14 na kasar a lokaci guda.

Mataimakin firaministan gwamnatin wucin gadi ta kasar Masar kuma ministan kula da harkokin bada ilmin jami'a na kasar Hossam Eissa ya sanar da wannan labari a gun taron manema labaru da aka gudanar a wannan rana. Kana ya bayyana cewa, za a ci gaba da daukar matakan kiyaye tsaro bayan da aka soke halin dokar ta baci.

A ranar 14 ga watan Agusta na bana, hukumar kasar Masar ta murkushe sansanin magoya bayan Mohamed Morsy, lamarin da ya kai ga aza dokar ta baci har na tsawon wata daya a dukkan kasar, tana kuma kafa dokar hana fitar dare tun daga karfe 7 na dare zuwa karfe 6 na safe a kowace rana a jihohi 14 na kasar. A halin yanzu, ana aiwatar da dokar hana fitar dare daga karfe 1 zuwa karfe 5 na safe a kowace rana. Amma dalilin yawan samun zanga-zanga bayan kowace sallar juma'a, sai lokacin dokar a juma'ar ya canja a ranar tun daga karfe 7 na dare zuwa karfe 5 na safe. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China