in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi Allah wadai da harin ta'addanci da aka kai kan fararen hula da hukumomin gwamnati a Masar
2013-12-24 17:30:46 cri
A yau Talata 24 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin, Hua Chunying ta bayyana cewa, Sin ta nuna rashin jin dadin ta tare da yin Allah wadai da harin ta'addanci da aka kai wa fararen hula da hukumomin gwamnati a kasar Masar.

Da ta ke bayani ga manema labarai a nan birnin Beijing Madam Hua tace Sin na fatan za a tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a kasar nan bada dadewa ba.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, a safiyar yau, boma-boman da aka dasa cikin mota a dab da wani babban ofishin 'yan sanda a garin Mansoura dake arewacin kasar Masar sun tashi inda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 14, yayin da wasu sama da dari suka jikkata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China