in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi kira ga bangarorin Sudan ta Kudu da su hau teburin shawara
2013-12-21 17:23:42 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya fidda wata sanarwa ga kafofin watsa labarai, wadda ke kunshe da nuna matukar damuwa, ga tabarbarewar yanayin tsaro a kasar Sudan ta Kudu, tare da suka mai tsanani kan hare-haren da aka kai wa sojojin kiyaye zaman lafiyar majalissar da ma jama'ar kasa.

Sanarwar ta kuma yi kira ga bangarorin mabanbanta dake kasar, da su dakatar da rura wutar rikici, su kuma rungumi shawarwari a matsayin hanyar warware rikicin dake addabar kasar.

Bisa rahoton baya bayan nan da ya fito daga ofishin kakakin MDDr, an ce a ranar 19 ga wata, an kai wani hari sansanin rundunar musamman ta MDD dake kasar Sudan ta Kudu, harin da ya haddasa mutuwar fararen hula a kalla 11. Sabanin mutane 20 da a baya aka ce sun rasu sakamakon farmakin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China