in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya sun yi maraba da yarjejeniyar da aka cimma kan batun nukiliya na kasar Iran
2013-11-26 15:31:40 cri
A ranar Litinin 25 ga wata ne, kasashen duniya suka ci gaba da nuna maraba ga yarjejeniyar da kasashen shida da batun nukiliyar kasar Iran ya shafa da Iran din kanta suka cimma wajen warware batun nukiliya na kasar Iran a matakin farko.

Amma ba a soke takunkumin da aka sanyawa kasar Iran a yanzu ba.

Ministan harkokin waje na kasar Faransa Laurent Fabius ya bayyana wa wakilin gidan rediyon Europe 1 na kasar a wannan rana cewa, kungiyar EU za ta dage wasu takunkumin da ta sanyawa kasar Iran a wata mai zuwa, amma an kayyade matakan soke takunkumin, kuma watakila za ta canja kudurinta na ci gaba da sanya takunkumin. Kana ya ce, ita ma kasar Amurka za ta dauki irin wannan mataki.

Ban da wannan kuma, ministan harkokin waje na kasar Canada John Baird ya sanar da cewa, kasarsa za ta ci gaba da sanya takunkumi kan kasar Iran a dukkan fannoni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China