in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya gana da ministan harkokin wajen kasar Masar
2013-12-16 16:30:48 cri
A ranar Litinin din nan 16 ga wata, Mataimakin Shugaban kasar Sin Li Yuanchao ya gana da ministan harkokin wajen kasar Masar Nabil Fahmi a nan birnin Beijing,fadar gwamnatin kasar .

A lokacin ganawar Li Yuanchao ya ce, a cikin shekaru sama da 50 da suka gabata, bayan da Sin da Masar suka kulla dangantakar diflomasiya an gudanar da zumunci tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata, don haka kasar Sin take girmama zabin kasar jama'ar Masar game da tsarin siyasa da hanyar samun bunkasuwar su. Ya ce Sin tana kuma mai da hankali sosai game da dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare da ke tsakanin kasashen biyu tare da fatan kiyaye da fadada mu'amala da hadin gwiwa da kasar ta Masar.

A nasa bangare shi ma Nabil Fahmi ya yi bayani game da sabon yanayin da ake ciki a kasar Masar, inda ya ce, raya dangantakar da ke tsakaninta da Sin, ya zama zaben da Masar ta yi, kuma yana fatan ci gaba da inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da zurfafa mu'amala da hadin gwiwa a tsakanin su daga dukkan fannoni .(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China