in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane sama da 600 ne suka mutu sakamakon barkewar rikici a kasar Afirka ta Tsakiya, in ji hukumar UNHCR
2013-12-14 16:13:37 cri
Sama da mutane 600 ne suka rasa rayukan su, yayin da wasu sama da dubu 160 suka rasa matsugunni sakamakon rikicin da ya abku a makon jiya a kasar Afirka ta Tsakiya.

kakakin hukumar kula da harkokin 'yan gudun hijira ta MDD (UNHCR) Adrian Edwards ne ya bayyana hakan a jiya Jumma'a 13 ga wata, yayin wani taron 'yan jarida da aka shirya a birnin Geneva.

Mista Edwards ya ce, bisa alkaluman da kungiyar Red Cross ta kasar, da hukumar jin kai ta Denmark suka fitar, mutane sama da 450 ne suka mutu sakamakon rikicin da ya abku a birnin Bangui, hedkwatar kasar, yayin da wasu mutane sama da 160 suka mutu a sauran sassan kasar daban daban.

Dadin dadawa, mista Edwards ya kara da cewa, mutane kimanin dubu 159 sun tsere daga gidajen su sakamakon tashe tsahen hankulan da suka auku cikin makon jiya, yayin da wasu al'ummar kasar kimanin 1800 suka tsallaka zuwa Kongo Kinshasa da kuma Congo-Brazzaville domin tsira da rayukan su.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China