in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron kwamitin tsakiyar JKS kan aikin tattalin arziki a birnin Beijing
2013-12-13 20:41:26 cri
Daga ranar 10 zuwa 13 ga wata, aka yi taron kwamitin tsakiyar jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin kan tattalin arziki a nan birnin Beijing, inda aka nuna cewa, tsayawa tsayin daka kan neman ci gaba mai dorewa da yin kwaskwarima sun kasance aikin da za'a saka a gaba a shekara mai zuwa a fannin tattalin arziki,don haka kamata ya yi a kara samun fahimta kan dangantaka tsakanin neman samun dauwamammen ci gaba yadda ya kamata da karuwar GDP, da kokarin tabbatar da ingancin bunkasar tattalin arziki da samun moriya ba tare da kawo illa ba, da kuma ci gaba da gudanar da manufar kasafin kudi cikin yakini.

A cikin jawabinsa, babban darektan kwamitin tsakiyar JKS, kana shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi nazari kan yanayin da ake ciki a fannin tattalin arziki, da waiwaye game da aikin tattalin arziki a shekarar 2013, tare da gabatar da bukatu da manyan ayyuka a wannan fanni a badi. A nasa bangare kuma, firaministan kasar Li Keqiang ya yi jawabi kan manufar tattalin arziki daga manyan fannoni a badi tare da bayyana hakikanan matakan da za a dauka.

Dadin dadawa, a gun taron, an tabbatar da manyan ayyukan tattalin arzikin Sin guda shida da za'a maida hankali a kai a badi, wato ba da tabbaci ga ingancin abinci, kyautata tsarin masana'antu, kula da matsalar basusuka, sa kaimi ga samun bunkasuwa a yankuna cikin daidaito, ba da tabbaci da kyautata rayuwar jama'a, da kuma kara bude kofa ga kasashen waje.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China