in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gano alamar sake bude na'urar sarrafa nukiliya dake birnin Yongbyon na Koriya ta Arewa
2013-11-29 10:38:02 cri
Jiya Alhamis 28 ga wata, yayin taron majalisar zartaswa da aka yi a birnin Vienna, babban sakataren hukumar makamashin nukiliyar ta kasa da kasa IAEA, Amano Yukiya ya bayyana cewa, hukumar na ganin cewa, akwai alamar sake bude na'urar sarrafa nukiliya dake birnin Yongbyon na kasar Koriya ta Arewa, ko da yake ya zuwa yanzu ba a iya tabbatar da hakan ba.

Mr. Amano ya bayyana cewa, hukumar ta gano alamar yayin da take binciken yanayin na'urar sarrafa nukiliya dake birnin Yongbyon ta hutunan taurarin dan Adam. Amma, sabo da ma'aikata masu bincike ba su iya shiga kasar ba, ba za a iya tabbatar da ko kasar ta riga ta sake bude na'urar sarrafa nukiliya, ko a'a ba. Bugu da kari, Mr. Amano ya bukaci kasar Koriya ta Arewa ta kiyaye ka'idojin da kwamitin tsaron MDD ya gindaya kan wannan batu, kuma ta fara yin hadin gwiwa tare da hukumar makamashin nukiliyar kasa da kasa don gudanar da bincike kan lamarin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China